Ya Allah, ka gafarta mini ka yi mani rahama, kuma ka riskar da ni da mafi girman abokin zama

Ya Allah, ka gafarta mini ka yi mani rahama, kuma ka riskar da ni da mafi girman abokin zama

Daga A’isha, Allah Ya yarda da ita, wacce ta ce: Na ji Annabi - Salatin Allah da amincin Allah su tabbata a gare shi - yayin da yake dogaro da ni, yana cewa: “Ya Allah, ka gafarta mini ka yi mani rahama, kuma ka riskar da ni da mafi girman abokin zama.”

[Ingantacce ne] [Bukhari da Muslim suka Rawaito shi]

الشرح

Lokacin da rayuwar Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ta kusanto, sai ya dogara da Uwar Muminai, A'isha - Allah ya yarda da ita - kamar yadda ya roki Ubangijinsa ya hada shi da sahabi, wato annabawa, masu gaskiya, shahidai da salihai.

التصنيفات

Wafatinsa SAW