إعدادات العرض
"Allah Madaukakin Sarki yana cewa: Ni ina tare da Bawa na ko yaushe ya anbace ni kuma Labbansa suka Motsa saboda ni"
"Allah Madaukakin Sarki yana cewa: Ni ina tare da Bawa na ko yaushe ya anbace ni kuma Labbansa suka Motsa saboda ni"
An karbo daga Abu Huraira -Allah ya yarda da shi- ya ce: Manzon Allah tsira da Amincin Allah su tabbata a gare shi- ya ce: "Allah Madaukakin Sarki yana cewa: Ni ina tare da Bawa na ko yaushe ya anbace ni kuma Labbansa suka Motsa saboda ni"
[Ingantacce ne ta wani bangaren] [Ibnu Majah ne ya Rawaito shi - Bukhari Ya Rawaito shi Mu'allak amma ta Sigar Yankewa - Ahmad ne ya rawaito shi]
الترجمة
العربية বাংলা Bosanski English Español فارسی Français Bahasa Indonesia Русский Tagalog Türkçe اردو 中文 हिन्दी සිංහල Kurdî Portuguêsالشرح
Hadisin yana nuna cewa duk wanda ya tuna Allah to Allah zai kasance kusa da shi, kuma zai kasance tare da shi a kowane Al-amuransa, Saboda zai datar da shi kuma ya shirye shi kuma ya taimake shi ya amsa Addu'arsa, kuma Ma'anar wannan Hadisin ta zo a cikin wani hadisin a cikin sahihul Bukhari Manzon Allah ya ce: "Ni ina inda Bawa na ya Zace ni kuma ni ina tare da shi a duk lokacin da ya anbaceni a , idan ya anbaceni cikin Ransa to zan anbace shi cikin raina, in kuma ya anbace ni cikin Mutane zan anbace shi cikin Mutanen da suka fi nasa Al-kairiالتصنيفات
Falalar Zikiri