إعدادات العرض
Iyalan (Annabi) Muhammad - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - basu taɓa ƙoshi daga abincin alkama a darare uku ajere ba tunda ya zo Madina, har aka karɓi ransa
Iyalan (Annabi) Muhammad - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - basu taɓa ƙoshi daga abincin alkama a darare uku ajere ba tunda ya zo Madina, har aka karɓi ransa
Daga Nana A'isha uwar muminai - Allah Ya yarda da ita - ta ce: Iyalan (Annabi) Muhammad - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - basu taɓa ƙoshi daga abincin alkama a darare uku ajere ba tunda ya zo Madina, har aka karɓi ransa.
[Ingantacce ne] [Bukhari da Muslim suka Rawaito shi]
الترجمة
العربية Português دری Македонски Magyar Tiếng Việt ქართული বাংলা Kurdî ไทย অসমীয়া Nederlands Bahasa Indonesia ਪੰਜਾਬੀ Kiswahiliالشرح
Uwar muminai Nana A'isha - Allah Ya yarda da ita - tana bada labarin cewa iyalan gidan Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - tun lokacin da Annabi ya zo Madina basu taɓa ƙoshi da alkama ba tsawon kwana uku ajere har (Annabi) tsira da amincin Allah su tabbata agare shi ya koma ga Allah.فوائد الحديث
Bayanin abin da Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - yake a kansa shi da iyalansa na ƙarancin rayuwa, domin rayuwa (ta haƙiƙa ita ce ) rayuwar lahira.
Ibnu Hajar ya ce: Abin da yake a bayyane shi ne cewa dalilin rashin ƙoshinsu galibi ya kasance ne saboda ƙarancin abu a wurinsu, akan cewa su sun kasance sukan samu saidai suna fifita wasunsu ne akan kansu.
