Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - bai taɓa yaƙar wasu mutane ba har sai ya kirasu (zuwa ga Addini)

Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - bai taɓa yaƙar wasu mutane ba har sai ya kirasu (zuwa ga Addini)

Daga Abdullahi Ibnu Abbas - Allah Ya yarda da su - ya ce: Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - bai taɓa yaƙar wasu mutane ba har sai ya kirasu (zuwa ga Addini).

[Ingantacce ne] [رواه أحمد والبيهقي]

الشرح

Ibnu Abbas - Allah Ya yarda da su - ya bada labarin cewa Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - bai taɓa farawa da yaƙar wasu mutane ba har sai ya kirasu zuwa ga Musulunci a farko, idan ba su amsa kiransa ba sai ya yaƙe su.

فوائد الحديث

An sharɗanta kira zuwa ga Musulunci kafin yaƙi idan Musuluncin bai isa zuwa garesu ba.

Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya kasance yana kiransu zuwa Musulunci, idan sun ƙi sai ya bijiro musu da bada da jizya, idan sun ƙi sai ya yaƙesu, kamar yadda ya zo a cikin wasu hadisan daban.

Hikima a cikin yaƙi ita ce shigar mutane cikin Addinin Musulunci, ba wai kwaɗayi a kan bayinsu ko dukiyoyinsu da garuruwansu ba.

التصنيفات

Hukunce Hukunce da Mas'alolin Jahadi