إعدادات العرض
Idan ɗayanku ya shiga masallaci to ya yi wa Annabi salati kuma ya ce: Ya Allah Ka buɗe mini ƙofofin rahamarKa
Idan ɗayanku ya shiga masallaci to ya yi wa Annabi salati kuma ya ce: Ya Allah Ka buɗe mini ƙofofin rahamarKa
Daga Abu Huraira Allah - Ya yarda da shi - cewa Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi ya ce: «Idan ɗayanku ya shiga masallaci to ya yi wa Annabi salati kuma ya ce: Ya Allah Ka buɗe mini ƙofofin rahamarKa, idan kuma zai fita to ya yi wa Annabi sallama sannan ya ce: Ya Allah Ka tsareni daga Shaiɗan abin jefewa». (Riwayar) Hakim: «Idan zai fita to ya yi wa Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - sallama, sannan ya ce: Ya Allah Ka tsareni daga Shaiɗan abin jefewa».
الترجمة
العربية Português دری Македонски Magyar ქართული Tiếng Việt বাংলা Kurdî ไทย অসমীয়া Bahasa Indonesia Nederlands ਪੰਜਾਬੀ Kiswahili ភាសាខ្មែរالشرح
Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya shiryar da musulmi cewa idan ya yi nufin shiga masallaci ya yi wa Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - salati da faɗinsa: Ya Allah Ka yi tsira Ka yi aminci ga (Annabi) Muhammad, sannan ya ce: (Ya Allah Ka buɗe mini ƙofofin rahamarKa). Idan zai fita to ya yi wa Annabi salati sai ya ce: (Ya Allah Ka tsareni daga Shaiɗan abin jefewa). A cikin riwayar Hakim: Sai ya ce: (Ya Allah Ka tsareni daga Shaiɗan abin jefewa).فوائد الحديث
An so wannan adddu'ar a yayin shiga masallaci da fita daga cikinsa.
Gamamman Zikirin ne a kowanne masallaci har Masallaci mai alfarma.
Keɓance ambatan rahama da shiga, da kuma tsari daga Shaiɗan a fita: Cewa mai shiga zai shagaltu da abin da zai kusanto da shi zuwa ga Allah da kuma aljannarSa sai ya dace da ya ambaci rahama, idan zai fita to shi zai shiga duniya da abin da ke cikinta na abubuwan shagaltarwa, sai ya dace da ya nemi kariya da kiyayewar Allah daga Shaiɗan.
التصنيفات
Hukunce Hukuncen Masallaci