إعدادات العرض
Duk mutumin da ya halarci (yaƙin) Badar da Hudaibiyya ba zai shiga wuta ba
Duk mutumin da ya halarci (yaƙin) Badar da Hudaibiyya ba zai shiga wuta ba
Daga Jabir - Allah Ya yarda da shi - ya ce: Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya ce: "Duk mutumin da ya halarci (yaƙin) Badar da Hudaibiyya ba zai shiga wuta ba".
[Ingantacce ne] [Ahmad ne ya rawaito shi]
الترجمة
العربية Bosanski English فارسی Bahasa Indonesia Русский 中文 हिन्दी ئۇيغۇرچە اردو Español Kurdî Français Português Tiếng Việt Kiswahili Nederlands অসমীয়া ગુજરાતી සිංහල Magyar ქართული Românăالشرح
Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya bada labarin cewa duk wanda ya halarci yaƙin Badar wanda aka yi a cikin shekara ta biyu da hijira yana mai yaƙi tare da Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi -, haka nan wanda ya halarci Sulhun Hudaibiyya, kuma a cikinsa ne aka yi Bai'atir Ridwan wacce aka yi a cikin shekara ta shida da hijira ba zai shiga wuta ba.فوائد الحديث
A cikinsa akwai falalar ma'abota (yaƙin) Badar da Hudaibiyya, kuma su ba zasu shiga wuta ba.
Bayanin cewa Allah - Maɗaukakin sarki - Zai lamunce musu abinda ake bin su, kuma Zai datar da su ga mutuwa akan imani, kuma Zai shigar da su aljanna ba tare da rigayar azabar wuta ba, wannan kuma falalar Allah ce da yake ba wa wanda Yake so, Allah Ma'abocin falala ne Mai girma.