"Akwai wani sarki a cikin waɗanda ke gabaninku, kuma ya kasance yana da wani matsafi*, lokacin da ya girma, sai ya cewa sarkin: Haƙiƙa ni na girma, ka aiko min da wani yaron da zan koya masa tsafi, sai ya aika masa da wani yaron da zai koya masa, ya kasance akan hanyarsa idan ya shiga akwai mai…

"Akwai wani sarki a cikin waɗanda ke gabaninku, kuma ya kasance yana da wani matsafi*, lokacin da ya girma, sai ya cewa sarkin: Haƙiƙa ni na girma, ka aiko min da wani yaron da zan koya masa tsafi, sai ya aika masa da wani yaron da zai koya masa, ya kasance akan hanyarsa idan ya shiga akwai mai ibada sai ya zauna a wurinsa ya ji zancensa, sai ya ƙayatar da shi, ya kasance idan zai zo wajen matsafin sai ya wuce ta wajen mai ibadar ya zauna a wurinsa, idan ya zo wajen matsafin sai ya dake shi, sai ya kai ƙarar hakan wajen mai ibadar, sai ya ce: Idan ka ji tsoron matsafin, to ka ce : Iyalaina ne suka tsareni, idan kuma ka ji tsoron iyalanka to ka ce: Matsafi ne ya tsareni. Yana cikin haka sai ga shi ya zo wajen wata babbar dabbar da ta tsare mutane, sai ya ce: A yau ne zan san cewa matsafi ne ya fi ko mai ibada ne ya fi ? sai ya ɗauki wani dutse, sai ya ce: Ya Allah idan al'amarin mai ibadar ne shi ne mafi soyuwa gareKa to Ka kashe wannan dabbar, har mutane su tafi, sai ya jefeta sai ya kasheta, mutane suka wuce, sai ya zo wajen mai ibadar sai ya ba shi labari, sai mai ibadar ya ce masa: Ya kai ɗana kai a yau ka fini, haƙiƙa al'amarinka ya kai abinda ka gani, lallai cewa kai za'a jarrabeka, idan an jarrabeka to kada ka nuna ni, yaron ya kasance yana warkar da makaho da kuturu, kuma yana bawa mutane maganin sauran cututtuka, sai wani ɗan majalisar sarki wanda ya makance ya ji, sai ya zo masa da kyaututtuka masu yawa, sai ya ce: Abinda ke nan saboda kaine na tarasu, idan ka warkar da ni, sai ya ce: Ni bana warkar da wani, kawai Allah ne Yake warkarwa, idan ka yi imani da Allah zan roƙi Allah sai Ya warkar da kai, sai ya yi imani da Allah sai Allah Ya warkar da shi, sai ya zo wajen sarkin, sai ya zauna a wurinsa kamar yadda ya kasance yana zama, sai sarkin ya ce da shi: Waye ya dawo maka da ganinka? Ya ce: Ubangijina, ya ce: Shin kana da wani Ubangijin wanina? ya ce: Ubangijina kuma Ubangijinka Shi ne Allah, sai ya kama shi bai gushe ba yana ta azabtar da shi har saida ya nuna yaron, sai aka zo da yaron, sai sarkin ya ce masa: Yakai ɗana, haƙiƙa tsafinka ya kai har kana iya warkar da makaho da kuturu kana yin kaza da kaza?! sai ya ce: Ni bana warkar da wani, kawai Allah ne Yake warkarwa, sai ya kama shi bai gusheba yana azabtar da shi har sai da ya nuna mai ibadar, sai aka zo da mai ibadar sai aka ce masa: Ka bar Addinika, sai ya ƙi, sai ya sa aka kawo masa zarto sai ya ɗora zartan a tsakiyar kansa, sai ya tsaga shi har saida ɓarikan jikinsa biyu suka faɗi, sannan aka zo da ɗan majalisar sarki sai aka ce da shi: Ka bar Addininka, sai ya ƙi, sai aka ɗora zarton akan tsakiyar kansa, sai ya tsaga shi da shi har sai da ɓangarorin jnikinsa biyu suka faɗi, sannan aka zo da yaron sai aka ce da shi: Ka bar Addininka, sai ya ƙi, sai ya miƙa shi wurin wasu jama'a daga mutanensa, sai ya ce: Ku tafi da shi zuwa dutsen kaza da kaza, ku hau dutsen da shi, idan kun kai ƙololuwarsa idan ya bar Addininsa to (ku kyale shi) inba haka ba fa to ku jeho shi, sai suka tafi da shi zuwa dutsen kaza da kaza sai suka hau dutsen da shi, sai ya ce: Ya Allah ka isar mini su da abinda Ka so, sai dutsen ya girgiza da su sai suka faɗo, sai ya zo yana tafiya zuwa wurin sarkin, sai sarkin ya ce da shi: Me mutanenka suka yi? sai ya ce: Allah Ya isar mini su, sai ya ƙara bada shi ga wasu daga cikin mutanensa sai ya ce: Ku tafi da shi ku ɗauke shi a cikin jirgin ruwa, kuje tsakiyar kogi da shi, idan ya bar Addininsa to inba haka ba fa to ku jefa shi, sai suka tafi da shi, sai ya ce: Ya Allah ka isar mini su da abinda Ka so, sai jirgin ruwan ya kife da su sai suka dilmiye, sai ya zo yana tafiya wurin sarkin, sai sarkin ya ce da shi: Me mutanenka suka yi? sai ya ce: Allah Ya isar mini su, sai ya cewa sarkin: Kai ba zaka iya kasheni ba har sai ka aikata abinda zan umarceka da shi, ya ce: Menene shi? ya ce: Ka tara mutane wuri ɗaya ka tsireni akan wani kututture, sannan ka ɗauki wani mashi daga cikin kibiyoyina, sannan ka sanya mashin a tsakiyar gwafa sannan ka ce: Da sunan Allah Ubangijin yaro, sannan ka harbeni, lallai kai idan ka aikata hakan to zaka kasheni, sai ya tara mutane a wuri ɗaya, sai ya tsire shi akan wani kututture, sannan ya ɗauki wani mashi daga cikin kibiyoyinsa sannan ya sanya mashin a cikin tsakiyar gwafa, sannan yace: Da sunan Allah Ubangijin yaro, sannan ya harbe shi sai ya faɗi ta kayakayinsa, sai ya ɗora hannunsa akan kayakayinsa sai ya mutu, sai mutane suka ce: Mun yi imani da Ubangijin yaro, sai aka zo wa sarkin sai aka ce da shi: Shin kana ganin abinda tsoro, haƙiƙa wallahi tsoronka ya faru, mutane sun yi imani, sai ya yi umarni da haƙa rami ta farkon layuka sai aka haƙa kuma aka hura wuta a cikinsu kuma ya ce: Duk wanda bai bar Addininsa ba to ku cusa shi a cikinta, ko a ce masa: Ka faɗa sai suka aikata, har sai da wata mace ta zo alhali a tare da ita akwai wani ɗanta ƙarami, sai ta tsaya taƙi kutsawa ciki, sai ɗan nata ya ce mata: Ya babata ki yi haƙuri lallai cewa ke akan gaskiya kike".

Daga Suhaib - Allah Ya yarda da shi - cewa Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya ce: "Akwai wani sarki a cikin waɗanda ke gabaninku, kuma ya kasance yana da wani matsafi, lokacin da ya girma, sai ya cewa sarkin: Haƙiƙa ni na girma, ka aiko min da wani yaron da zan koya masa tsafi, sai ya aika masa da wani yaron da zai koya masa, ya kasance akan hanyarsa idan ya shiga akwai mai ibada sai ya zauna a wurinsa ya ji zancensa, sai ya ƙayatar da shi, ya kasance idan zai zo wajen matsafin sai ya wuce ta wajen mai ibadar ya zauna a wurinsa, idan ya zo wajen matsafin sai ya dake shi, sai ya kai ƙarar hakan wajen mai ibadar, sai ya ce: Idan ka ji tsoron matsafin, to ka ce : Iyalaina ne suka tsareni, idan kuma ka ji tsoron iyalanka to ka ce: Matsafi ne ya tsareni. Yana cikin haka sai ga shi ya zo wajen wata babbar dabbar da ta tsare mutane, sai ya ce: A yau ne zan san cewa matsafi ne ya fi ko mai ibada ne ya fi ? sai ya ɗauki wani dutse, sai ya ce: Ya Allah idan al'amarin mai ibadar ne shi ne mafi soyuwa gareKa to Ka kashe wannan dabbar, har mutane su tafi, sai ya jefeta sai ya kasheta, mutane suka wuce, sai ya zo wajen mai ibadar sai ya ba shi labari, sai mai ibadar ya ce masa: Ya kai ɗana kai a yau ka fini, haƙiƙa al'amarinka ya kai abinda ka gani, lallai cewa kai za'a jarrabeka, idan an jarrabeka to kada ka nuna ni, yaron ya kasance yana warkar da makaho da kuturu, kuma yana bawa mutane maganin sauran cututtuka, sai wani ɗan majalisar sarki wanda ya makance ya ji, sai ya zo masa da kyaututtuka masu yawa, sai ya ce: Abinda ke nan saboda kaine na tarasu, idan ka warkar da ni, sai ya ce: Ni bana warkar da wani, kawai Allah ne Yake warkarwa, idan ka yi imani da Allah zan roƙi Allah sai Ya warkar da kai, sai ya yi imani da Allah sai Allah Ya warkar da shi, sai ya zo wajen sarkin, sai ya zauna a wurinsa kamar yadda ya kasance yana zama, sai sarkin ya ce da shi: Waye ya dawo maka da ganinka? Ya ce: Ubangijina, ya ce: Shin kana da wani Ubangijin wanina? ya ce: Ubangijina kuma Ubangijinka Shi ne Allah, sai ya kama shi bai gushe ba yana ta azabtar da shi har saida ya nuna yaron, sai aka zo da yaron, sai sarkin ya ce masa: Yakai ɗana, haƙiƙa tsafinka ya kai har kana iya warkar da makaho da kuturu kana yin kaza da kaza?! sai ya ce: Ni bana warkar da wani, kawai Allah ne Yake warkarwa, sai ya kama shi bai gusheba yana azabtar da shi har sai da ya nuna mai ibadar, sai aka zo da mai ibadar sai aka ce masa: Ka bar Addinika, sai ya ƙi, sai ya sa aka kawo masa zarto sai ya ɗora zartan a tsakiyar kansa, sai ya tsaga shi har saida ɓarikan jikinsa biyu suka faɗi, sannan aka zo da ɗan majalisar sarki sai aka ce da shi: Ka bar Addininka, sai ya ƙi, sai aka ɗora zarton akan tsakiyar kansa, sai ya tsaga shi da shi har sai da ɓangarorin jnikinsa biyu suka faɗi, sannan aka zo da yaron sai aka ce da shi: Ka bar Addininka, sai ya ƙi, sai ya miƙa shi wurin wasu jama'a daga mutanensa, sai ya ce: Ku tafi da shi zuwa dutsen kaza da kaza, ku hau dutsen da shi, idan kun kai ƙololuwarsa idan ya bar Addininsa to (ku kyale shi) inba haka ba fa to ku jeho shi, sai suka tafi da shi zuwa dutsen kaza da kaza sai suka hau dutsen da shi, sai ya ce: Ya Allah ka isar mini su da abinda Ka so, sai dutsen ya girgiza da su sai suka faɗo, sai ya zo yana tafiya zuwa wurin sarkin, sai sarkin ya ce da shi: Me mutanenka suka yi? sai ya ce: Allah Ya isar mini su, sai ya ƙara bada shi ga wasu daga cikin mutanensa sai ya ce: Ku tafi da shi ku ɗauke shi a cikin jirgin ruwa, kuje tsakiyar kogi da shi, idan ya bar Addininsa to inba haka ba fa to ku jefa shi, sai suka tafi da shi, sai ya ce: Ya Allah ka isar mini su da abinda Ka so, sai jirgin ruwan ya kife da su sai suka dilmiye, sai ya zo yana tafiya wurin sarkin, sai sarkin ya ce da shi: Me mutanenka suka yi? sai ya ce: Allah Ya isar mini su, sai ya cewa sarkin: Kai ba zaka iya kasheni ba har sai ka aikata abinda zan umarceka da shi, ya ce: Menene shi? ya ce: Ka tara mutane wuri ɗaya ka tsireni akan wani kututture, sannan ka ɗauki wani mashi daga cikin kibiyoyina, sannan ka sanya mashin a tsakiyar gwafa sannan ka ce: Da sunan Allah Ubangijin yaro, sannan ka harbeni, lallai kai idan ka aikata hakan to zaka kasheni, sai ya tara mutane a wuri ɗaya, sai ya tsire shi akan wani kututture, sannan ya ɗauki wani mashi daga cikin kibiyoyinsa sannan ya sanya mashin a cikin tsakiyar gwafa, sannan yace: Da sunan Allah Ubangijin yaro, sannan ya harbe shi sai ya faɗi ta kayakayinsa, sai ya ɗora hannunsa akan kayakayinsa sai ya mutu, sai mutane suka ce: Mun yi imani da Ubangijin yaro, sai aka zo wa sarkin sai aka ce da shi: Shin kana ganin abinda tsoro, haƙiƙa wallahi tsoronka ya faru, mutane sun yi imani, sai ya yi umarni da haƙa rami ta farkon layuka sai aka haƙa kuma aka hura wuta a cikinsu kuma ya ce: Duk wanda bai bar Addininsa ba to ku cusa shi a cikinta, ko a ce masa: Ka faɗa sai suka aikata, har sai da wata mace ta zo alhali a tare da ita akwai wani ɗanta ƙarami, sai ta tsaya taƙi kutsawa ciki, sai ɗan nata ya ce mata: Ya babata ki yi haƙuri lallai cewa ke akan gaskiya kike".

[Ingantacce ne] [Muslim ne ya rawaito shi]

الشرح

Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya bada labarin cewa akwai wani sarki cikin waɗanda suka gabacemu daga cikin al’ummu, ya kasance yana da wani matsafi, lokacin da matsafin ya girma (ya tsufa), sai ya cewa sarkin: Lallai ni na girma, to ka aiko wani saurayi zuwa wurina in koya masa tsafi. Sai sarkin ya aika masa da wani saurayin da zai koya masa, a kan hanyar saurayin idan zai tafi gurin matsafin akwai wani mai ibada, sai ya zauna a wurinsa sau ɗaya ya ji zancensa, sai ya ƙayatar da shi. Ya kasance idan ya zo wurin matsafin sai ya wuce wurin mai ibadar ya zauna a wurinsa, idan kuma ya je wurin matsafin sai ya dake shi, saboda jinkirin da ya yi, sai ya kai ƙarar hakan wurin mai ibadar, sai ya ce: Idan ka ji tsoron matsafin, to ka ce: Iyalaina ne suka tsareni, idan kuma ka ji tsoron iyalanka to ka ce : Matsafi ne ya tsareni. Sun kasance a haka lokacin da ya zo wa wata babbar dabba ta hana mutane wucewa, sai ya ce: A yau ne zan san cewa matsafi ne ya fi ko kuma mai ibada ne yafi? Sai ya ɗauki wani dutse, sai ya ce: Ya Allah idan al'amarin wannan mai ibadar ne mafi soyuwa gareKa daga al'amarin matsafin nan to Ka kashe wannan dabbar, har mutane su wuce, sai ya jefeta sai ya kasheta, kuma mutane suka wuce, sai ya zo wajen mai ibadar sai ya ba shi labari, sai mai ibadar ya ce masa: Ya kai ɗana ! Kai a yau ka fini, haƙiƙa al'amarinka ya kai abinda kake gani, kuma lallai za'a jarrabeka, idan an jarrabeka to kada ka nuna ni, yaron ya kasance yana warkar da makaho da kuturu, yana bawa mutane maganin sauran cututtuka da izinin Allah, sai wani ɗan majalisar sarki wanda ya rasa idonsa ya ji, sai ya zo masa da kyautuka masu yawa, sai ya cewa yaron: Dukkan abinda ke nan na kyautuka naka ne idan ka warkar da ni. Sai ya ce: Lallai ni bana warkar da wani kawai Allah ne Yake warkarwa, idan ka ni imani da Allah zan roƙi Allah Ya warkar da kai, sai ya yi imani da Allah sai Allah Ya warkar da shi, sai ya zo wajen sarkin sai ya zauna a wurinsa kamar yadda ya kasance yake zama, sai sarkin ya ce masa: Waye ya mayar maka da ganinka? Ya ce: Ubangijina, ya ce: Shin kana da wani Ubangijin wanina? Ya ce: Ubangijina da Ubangijinka shi ne Allah. Sai ya kama shi bai gushe ba yana azabtar da shi har sai da ya nuna yaron, sai aka zo da yaron, sai sarkin ya ce masa: Ya kai ɗana ! haƙiƙa tsafinka yakai har kana warkar da makaho da kuturu, kana aikata kaza da kaza. Sai ya ce: Ni bana warkar da wani, kawai Allah ne Yake warkarwa, sai ya kama shi bai gushe ba yana azabtar da shi har saida ya nuna mai ibadar. Sai aka zo da mai ibadar, sai aka ce da shi: Ka bar Addininka, sai yaƙi, sai ya ce akawo masa zarto, sai ya ɗora shi akan tsakiyar kansa, sai ya raba shi gida biyu. Sannan aka zo da ɗan majalisar sarkin sai aka ce da shi: Ka bar Addininka, sai ya ƙi sai ya sanya zarto akan tsakiyar kansa, sai ya raba shi gida biyu. Sannan aka zo da yaron sai aka ce masa ka bar Addinika, sai ya ƙi sai ya miƙashi wurin wasu mazaje daga mutanensa tsakanin uku da goma. Sai ya ce: Ku tafi da shi zuwa dutsen kaza da kaza, ku hau dutsen da shi, idan kun kai ƙololuwarsa, idan ya bar Addininsa to, inba haka bafa to ku jeho shi, sai suka tafi da shi sai suka hau dutsen da shi. Sai yaron ya ce: Ya Allah ka isar mini su da abinda Ka so, sai dutsen ya girgiza da su ya yi motsi motsi mai tsanani sai suka faɗo, sai ya zo yana tafiya zuwa wurin sarkin. Sai sarkin ya ce masa: Me mutanenka suka yi? Ya ce: Allah Ya isar mini su. Sai ya miƙashi zuwa wasu mutane daga cikin mutanensa, sai ya ce: Ku tafi da shi ku ɗaukeshi a cikin ƙaramin jirgin ruwa, sai ku tafi tsakiyar kogi da shi, idan ya bar Addininsa (ku kyale shi) inba haka ba fa to ku jefa shi a cikin kogin. Sai suka tafi da shi, sai ya ce: Ya Allah Ka isar mini su da abinda Ka so, sai jirgin ruwan ya kife da su sai suka dilmiya, sai ya zo yana tafiya wurin sarkin. Sai sarkin ya ce masa: Me mutanenka suka yi? Sai ya ce: Allah Ya isar mini su, sai yaron ya cewa sarkin: Lallai cewa kai ba zaka iya kasheni ba har sai ka aikata abinda zan umarceka da shi. Ya ce: Menene shi? Ya ce: Ka tara mutane a babban fili, ka tsireni akan kututturen bishiya, sannan ka ɗauki wani mashi daga cikin kibiyoyina, sannan ka sanya mashin a tsakiyar kwari, sannan ka ce: Da sunan Allah Ubangijin yaro, sannan ka harbeni, lallai cewa kai idan ka aikata haka to zaka kasheni, sai ya tara mutane a wuri ɗaya, ya tsire shi akan wani kututture, sannan ya ɗauki wani mashi daga cikin kibiyoyinsa, sannan ya sanya mashin a tsakiyar kwari, sannan ya ce: Da sunan Allah Ubangijin yaro, sannan ya harbe shi sai mashin ya faɗa a kayakayinsa tsakanin idanuwansa da kunnansa, sai ya ɗora hannunsa a kayakayinsa a wurin da mashin (ya faɗa) sai ya mutu. Sai mutane suka ce: Mun yi imani da Ubangijin yaro, mun yi imani da Ubangijin yaro, Mun yi imani da Ubangijin yaro. Sai aka zo wa sarkin aka ce masa: Shin kaga abinda ka kasance kana jin tsoro? Haƙiƙa wallahi abinda ka ji tsoro ya kasance, shi ne mutane suna bin yaron da yin imani da Ubangijin yaron bakiɗayansu, sai ya yi umarni a tsaga ƙasa a yi manyan ramuka masu tsawo a ƙofofin hanyoyi, aka kunna wuta a cikinsu, kuma ya ce: Duk wanda bai bar Addininsa ba to ku jefa shi a cikinta, sai suka aikata abinda sarkin ya umarcesu da shi, har wata mace ta zo atare da ita akwai wani ɗanta ƙarami, sai ta tsaya ta lazimci inda take, taƙi shiga cikin wutar, sai ɗanta ya ce mata: Ya babata ki yi haƙuri, lallai ke akan gaskiya kike.

فوائد الحديث

Tabbatar da karamomin waliyyai, daga cikin hakan akwai kashe babbar dabba ta hanyar jifan yaron, da kuma amsa addu'ar yaron sau biyu, da kuma maganar ƙaramin yaron da ake shayar da shi.

Taimakon wanda ya dogara ga Allah - tsarki ya tabbatar maSa -.

Bayanin matsayin haƙuri da kuma tabbata akan Addini.

Hikima a cikin neman ilimi a farkon rayuwa; domin cewa saurayi a galibi ya fi saurin hadda akan babba.

Ƙarfin imanin wannan yaron, kuma cewa bai yi nisa da imaninsa ba bai kuma juya baya ba.

Allah - Mai girma da ɗaukaka - Yana amsa kiran wanda ke cikin tsananin buƙata idan ya kiraShi.

Mutum yana halatta ya ruɗar da kansa a cikin maslahar dukkanin musulmai, domin wannan yaron ya nunawa sarki abinda zai kashe shi da shi ya kuma halakar da kansa da shi, shi ne ya ɗauki mashi daga cikin kibiyoyinsa ya sanya shi a tsakiyar kwari sai ya ce: Da sunan Allah Ubangijin yaro.

Halaccin yin ƙarya a cikin yaƙi da makamancinsa, da kuma tsamo rai daga halaka.

Mumini ana jarrabarsa a cikin gaskiyar imaninsa da kuma tabbata akan faɗin gaskiya, ko da al'amarin zai kaishi ga rasa ransa.

Bada rai ta hanyar kira zuwa ga Allah da kuma bayyanar da gaskiya.

Zukatan bayi suna hannun Allah Yana shiryar da wanda Yake so kuma Yana ɓatar da wanda Ya ga dama, haƙiƙa yaron ya shiriya alhali shi yana karkashin renon matsafi da kuma kulawar sarki mai laifi.

Halaccin roƙon Allah - Maɗaukakin sarki - Ya nunawa bawa alamar da zai san daidai, da ita kuma yaƙini ya tabbata gare shi .

Masu imani suna bada dukkan abinda Allah Ya basu kuma Ya yi musu falala da shi dan yi wa Addininsa hidima da kuma kira zuwa ga tarkinSa.

Sabubban halaka suna hannun Allah, idan Ya so sai Ya zartar da su idan kuma ya so sai ya yanke su.

Kafirai hujjoji da dalilai basa tauyesu dan yin imani, kawai sababin kafircinsu shi ne shisshigi da kuma girman kai.

Ɗagutai da azzalumai akwai suna da tanadi dan kashe mutane bakiɗaya dan su wanzu akan abinda suke a cikinsa na ni'imar duniya.

Allah Yana yi wa azzalumai uƙuba ta inda basa zato, haƙiƙa mutane sun yi imani da Ubangijin yaro lokacin da suka ga tabbatarsa da gaskiyar da'awarsa da kuma rashin tsoronsa ga zargin mai zargi saboda Allah.

Akwai waɗanda suka yi magana suna tsumman goyo banda (Annabi) Isa - aminci ya tabbata agare shi -, wannan hadisin yana bayanin faɗin Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi -: "Babu waɗanda suka yi magana a cikin shinfiɗar goyo sai mutum uku...", sai ya ambacesu, ya kuma taƙaitasu a cikin Banu Isra'il banda wasunsu.

التصنيفات

Tarihin Masu kira da Ayyukansu, Qissosi da labaran Al-umman da suka gabata