Na rantse da wanda raina yake a hannunsa zaku bi hanyar wadanda ke gabaninku

Na rantse da wanda raina yake a hannunsa zaku bi hanyar wadanda ke gabaninku

Daga Abu Wakid Al-Laisi - Allah Ya yarda da shi -: Cewa Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - lokacin da ya fita zuwa Hunain ya wuce wata bishiya ta mushrikai ana ce mata: Ma'abociyar rataya, suna rataye makamansu akanta, sai suka ce: Ya Manzon Allah, ka sanya mana ma'abociyar rataya kamar yadda suke da ma'abociyar rataya, sai Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce: "Tsarki ya tabbata ga Allah! wannan kamar yadda mutanen Musa sukace ne: {Ka sanya mana wani ubangiji kamar yadda suke da iyayen giji} [Al-Aaraf: 138] Na rantse da wanda raina yake a hannunsa zaku bi hanyar wadanda ke gabaninku".

[Ingantacce ne] [Al-Tirmithi Ya Rawaito shi]

الشرح

Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya fita zuwa Hunain shi: Wani kwari ne tsakanin Makka da Da’if, Ya kasance a tare da shi akwai wasu daga sahabban da ba su dade da shiga Musulunci ba. sai suka wuce wata bishiya ana ce mata: "Ma'abociyar rataya", wato: Ma'abociyar rataye-rataye, mushirikai sun kasance suna girmamata kuma suna rataya makamansu akanta da wasunsu dan neman albarka (sa’a). sai suka nema daga Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya sanya musu wata bishiyar irinta, za su dinga rataya makamansu akanta, dan neman albarka (sa’a), Dan zatonsu cewa wannan al'amarin ya halatta, sai Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya yi tasbihi dan inkarin wannan maganar, da kuma girmama Allah, kuma ya sanar da cewa wannan maganar ta yi kama da maganar mutanen (Annabi) Musa da suka ce da shi: {Ka sanya mana wani ubangiji kamar yadda suke da iyayen giji}, lokacin da suka ga wanda yake bautawa gumaka sai suka nemi ya zama suna da gumaka kamar yadda mushrikai suke da gumaka, kuma cewa wannan bin hanyar hanyarsu ne, sannan tsira da amincin Allah su tabbata agare shi ya bada labarin cewa wannan al'ummar za ta bi hanyar Yahudawa da Nasara kuma za ta aikata irin aikinsu, dan gargadarwa akan hakan.

فوائد الحديث

Mutum yakan ga kyan abu yana zatan cewa zai kusantar da shi zuwa ga Allah - Madaukakin sarki - alhali shi zai nisantar da shi daga Allah ne.

Ya kamata ga musulmi ya tsarkake Allah ya yi kabbara idan ya ji abinda ba ya kamata a fada a Addini, da kuma lokacin mamaki.

Yana daga shirka neman albarka daga bishiyoyi da duwatsu da wasunsu, ana neman albarka ne kawai daga Allah Shi kadai.

Sababin bautar gumaka shi ne girmamasu, da lazimtuwa a gurinsu, da neman albarka da su.

Wajabcin toshe kofofi da hanyoyin da za su kai zuwa ga shirka.

Abinda ya zo daga nassosi a zargin Yahudawa da Nasara to gargadi ne garemu.

Hani daga kamanceceniya da mutanen Jahiliyya da Yahudawa da Nasara, sai abinda dalili ya tabbatar akan shi yana daga Addininmu.

التصنيفات

Tauhidin Uluhiyya