إعدادات العرض
Idan ka kasance kamar yadda ka faɗa, to, kamar kana cusa musu toka mai zafi ne a bakin su, kuma wani mai rinjaye a kansu daga Allah ba zai gushe tare da kai ba muddin dai ka kasance a kan haka
Idan ka kasance kamar yadda ka faɗa, to, kamar kana cusa musu toka mai zafi ne a bakin su, kuma wani mai rinjaye a kansu daga Allah ba zai gushe tare da kai ba muddin dai ka kasance a kan haka
Daga Abu Huraira - Allah Ya yarda da shi -: Cewa wani mutum ya ce: Ya manzon Allah, ina da wasu 'yan uwa ina sadar musu (da zumunci), su kuma suna yanke mini, ina kyautata musu, su suna munanawa a gareni, ina haƙuri da su, su kuma suna yi min wauta, sai ya ce: "Idan ka kasance kamar yadda ka faɗa, to, kamar kana cusa musu toka mai zafi ne a bakin su, kuma wani mai rinjaye a kansu daga Allah ba zai gushe tare da kai ba muddin dai ka kasance a kan haka".
الترجمة
العربية বাংলা Bosanski English Español فارسی Français Bahasa Indonesia Русский Tagalog Türkçe اردو 中文 हिन्दी Tiếng Việt සිංහල Kurdî Kiswahili Português தமிழ் Nederlands অসমীয়া ગુજરાતી አማርኛ پښتو ไทย മലയാളം नेपालीالشرح
Wani mutum ya kai kuka wurin Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - cewa shi yana da makusanta da 'yan zumunci yana yi musu kyakkyawar mu'amala su kuma suna yi masa kishiyar haka; sai ya sadar da (zumuncin) su ya zo musu alhali su kuma suna yanke masa (zumunci), yana kyautata musu da yin aikin alheri da cika alƙawari su kuma suna munana masa da zalinci da wauta, yana yi musu haƙuri yana yi musu afuwa, su kuma suna yi masa wauta da mummunar magana da mummunan aiki, shin zai ci gaba da sadar musu (da zumunci) tare da abinda aka anbata? Sai Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce masa: Idan abinda ka faɗa haka yake to lallai cewa kai kana kunyatasu kuma kana wulaƙantasu akan kansu, kamar cewa kai kana ciyar da su toka ce mai zafi; dan yawan kyautatawarka da kuma mummunan aikinsu daga garesu, kuma wani mai taimakonka a kansu daga Allah, kuma mai tunkuɗe maka cutarsu akan abinda ka anbata na kyautatawarka garesu ba zai gushe tare da kai ba, su kuma su ci gaba akan munanawarsu gareka.فوائد الحديث
Fuskantar munanawa da kyautatawa zatan dawowar mai munanawar ne zuwa gaskiya, kamar yadd sa Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce: {Ka tunkuɗe da abinda yake shi ne mafi kyau sai ga wanda tsakaninka da tsakaninsa akwai adawa kamar shi masoyi ne mai tsananin soyayya}.
Riko da umarnin Allah koda wata cuta ta faru gare shi sababine na taimakon Allah ga bawa mumini.
Yanke zumunci raɗaɗine da azaba a duniya, kuma laifi ne da hisabi a lahira.
Yana kamata ga musulmi ya nemi lada a cikin aikinsa na gari, kada cutar mutane da yankewarsu ta hana shi daga al'adarsa mai kyau.
Wanda zai yi wa wanda ya sadar masa (da zumunci) sakayya bai zama mai sada (zumunci ba), saidai mai sadarwa a haƙiƙa shi ne wanda idan an yanke zumuncinsa zai sadar da shi.
التصنيفات
Falalar Sadar da zumunci