إعدادات العرض
Wanda Allah Yake nufinsa da alheri zai shafeshi da rashin lafiya (zai jarrabeshi)
Wanda Allah Yake nufinsa da alheri zai shafeshi da rashin lafiya (zai jarrabeshi)
Daga Abu Huraira - Allah Ya yarda da shi - ya ce: Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya ce: "Wanda Allah Yake nufinsa da alheri zai shafeshi da rashin lafiya (zai jarrabeshi)".
[Ingantacce ne] [Buhari ne ya rawaito shi]
الترجمة
العربية বাংলা Bosanski English Español فارسی Français Bahasa Indonesia Русский Tagalog Türkçe اردو 中文 हिन्दी Tiếng Việt සිංහල ئۇيغۇرچە Kurdî Português മലയാളം မြန်မာ Deutsch 日本語 پښتو অসমীয়া Shqip Svenska Čeština ગુજરાતી አማርኛ Yorùbá Nederlands తెలుగు Kiswahili தமிழ் ไทย دری Fulfulde Magyar Italiano ಕನ್ನಡ Кыргызча Lietuvių Malagasy or Română Kinyarwanda Српски тоҷикӣ O‘zbek Moore नेपाली Oromoo Wolof Soomaali Български Українська Azərbaycan bm ქართული Македонскиالشرح
Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - yana ba da labarin cewa idan Allah Ya yi nufin wani alheri ga bayinsa muminai sai ya jarrabesu a kawunansu da dukiyoyinsu, don abin da zai faru ga mumini na komawa zuwa ga Allah - Maɗaukakin sarki - da addu'a, da kankare munanan ayyuka, da ɗaukaka darajoji.فوائد الحديث
Lallai mumini abin bijirarwa ne ga nau'o'in bala'i.
Jarrabawa za ta iya kasancewa alama ce ta son Allah ga bawansa, har sai ya daukaka darajarsa, ya ɗaga martabarsa, ya kuma kankare laifinsa.
Kwaɗaitarwa a kan haƙuri a lokacin masifu da rashin ƙorafi.