Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya cewa Abubakar da Umar: "Waɗannan biyun sune shugabannin dattijan 'yan aljanna daga na farko dana ƙarshe sai dai Annabwa da Manzanni

Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya cewa Abubakar da Umar: "Waɗannan biyun sune shugabannin dattijan 'yan aljanna daga na farko dana ƙarshe sai dai Annabwa da Manzanni

Daga Anas - Allah Ya yarda da shi - ya ce: Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya cewa Abubakar da Umar: "Waɗannan biyun sune shugabannin dattijan 'yan aljanna daga na farko dana ƙarshe sai dai Annabwa da Manzanni".

[Ingantacce ne] [Al-Tirmithi Ya Rawaito shi]

الشرح

Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya bada labarin cewa Abubakar Siddiƙ da Umar Faruƙ - Allah Ya yarda da su - sune mafifitan mutane bayan Annabawa, kuma mafifitan waɗanda suka shiga aljanna bayan Annabwa da Manzanni.

فوائد الحديث

Abubakar da Umar - Allah Ya yarda da su - sune mafifitan mutane bayan Annabawa da Manzanni.

A aljanna babu tsoho, kai, wanda zai shigeta ɗan shekara talatin da uku ne, abin nufi cewa sune shugabannin wanda ya mutu yana dattijo a duniya, ko kuma hakan izina ne na abinda suke akansa a duniya a lokacin wannan hadisin.

التصنيفات

Darajar Sahabbai-Amincin Allah a gare su-, Falalar Sahabbai -Allah yayarda da su-