Wanda ya yi yaƙi dan kalmar Allah ta zama maɗaukakiya, to shi ne sabo da Allah

Wanda ya yi yaƙi dan kalmar Allah ta zama maɗaukakiya, to shi ne sabo da Allah

Daga Abu Musa - Allah Ya yarda da shi - ya ce: An tambayi manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - game da mutumin da yake yaƙi dan jarumta, (da wanda) yake yaƙi dan ƙabilanci, (da wanda) yake yaƙi dan riya, wanne ne saboda Allah? sai manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce: "Wanda ya yi yaƙi dan kalmar Allah ta zama maɗaukakiya, to shi ne sabo da Allah".

[Ingantacce ne] [Bukhari da Muslim suka Rawaito shi]

الشرح

An tambayi annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - daga saɓanin manufofin masu yin yaƙi; wanda ya yi yaƙi dan jarumtaka ko ƙabilanci ko dan aga matsayinsa a cikin mutane ko wanin hakan, wannene saboda Allah? Sai annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya bada labarin cewa wanda ya yi yaƙi saboda Allah shi ne: Wanda ya yi yaƙi dan kalmar Allah ta zama ita ce maɗaukakiya.

فوائد الحديث

Asali a cikin gyaruwar ayyuka da ɓacinsu (ita ce) niyya da tsarkake aiki saboda Allah.

Idan manufa daga yaƙi ita ce ɗaukaka kalmar Allah, kuma wata manufar daban abar shara'antawa ta haɗu a cikinsa, kamar samun ganima, to shi ba ya cutarwa.

Kare maƙiya daga shiga garuruwa da mutuncin mata yana daga yaƙi saboda Allah.

Falalar da ta zo a cikin mayaƙa tana keɓantuwa ne ga wanda ya yi yaƙi dan kalmar Allah - Maɗaukakin sarki - ta zama ita ce maɗaukakiya.

التصنيفات

Ladaban Jihadi