إعدادات العرض
Idan kun ji kiran sallah, to ku fadi irin abinda ladani yake fada
Idan kun ji kiran sallah, to ku fadi irin abinda ladani yake fada
Daga Abu Sa'id Al-Khudri - Allah Ya yarda da shi - cewa Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce: "Idan kun ji kiran sallah, to ku fadi irin abinda ladani yake fada".
[Ingantacce ne] [Bukhari da Muslim suka Rawaito shi]
الترجمة
عربي বাংলা Bosanski English Español فارسی Français Bahasa Indonesia Русский Tagalog Türkçe اردو 中文 हिन्दी Tiếng Việt ئۇيغۇرچە Português Kurdî മലയാളം Kiswahili Svenska cs ગુજરાતી አማርኛ Yorùbá සිංහල ไทย پښتو অসমীয়া دری Кыргызча or rw so नेपाली ro Lietuvių mgالشرح
Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - yana kwadaitarwa akan amsa wa ladani a lokacin jinsa, hakan da mu fadi irin abinda yake fada, jumla da jumla, A yayin da ya yi kabbara sai mu yi kabbara a bayansa, a yayin da ya zo da shaida biyu, sai mu zo da su a bayansa. An togance lafazin: (Ku yi gaggawa zuwa sallah, ku yi gaggawa zuwa tsira) cewa za'a fada a bayansu: Babu dabara babu karfi sai ga Allah.فوائد الحديث
Zai bi ladani na biyu bayan karewar na farko, koda ladanan suna da yawa; dan gamewar hadisin.
Ya amsawa ladani a kowanne hali, indai ba ya kasance ne a bayan gida ko yana kan biyan bukatarsa ba.