Allah ba Ya duba zuwa surorinku da dukiyoyinku, sai dai Yana duba zuwa zukatanku da ayyukanku

Allah ba Ya duba zuwa surorinku da dukiyoyinku, sai dai Yana duba zuwa zukatanku da ayyukanku

Daga Abu Huraira - Allah Ya yarda da shi - ya ce: Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya ce: "Allah ba Ya duba zuwa surorinku da dukiyoyinku, sai dai Yana duba zuwa zukatanku da ayyukanku".

[Ingantacce ne] [Muslim ne ya rawaito shi]

الشرح

Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - yana bayyana cewa Allah - Tsarki ya tabbatar masa Ya ɗaukaka - ba Ya duba zuwa surorin bayi da jikkunasu, shin su kyawawa ne ko munana ne? shin su manya ne ko kananu ne? lafiyayyu ne ko marasa lafiya ne? Kuma ba Ya duba zuwa dukiyoyinsu, shin masu yawa ne ko kaɗan ne? Allah - Mai girma da daukaka - ba Ya kama bayinsa kuma ba Ya yi musu hisabi a kan waɗannan al'amuran da fifikon da ya ke cikinsu, sai dai Yana duba zuwa zukatansu da abin da ke cikinsu na tsoron Allah da sakankancewa, da gaskiya da ikhlasi, ko nufin riya da jiyarwa, yana duba zuwa ayyukansu ta bangaren gyaransu da ɓacinsu; sai Ya bayar da lada, kuma Ya yi sakayya a kansu.

فوائد الحديث

Kulawa da gyara zuciya, da tsarkaketa daga dukkanin wata siffa abar zargi.

Gyaran zuciya ta hanyar ikhlasi ne, gyaran aiki kuma ta hanyar bin Annabi ne - tsira da aminci su tabbata a gare shi -, su ne abin dubawa da lura a wurin Allah - Maɗaukakin sarki -.

Kada mutum ya ruɗu da dukiyarsa ko kyawunsa ko jikinsa ko wani abu daga abubuwan wannan duniyar.

Gargaɗi daga karkata zuwa zahiri ba tare da gyara baɗini ba.

التصنيفات

Tauhidin Sunaye da Siffofi, Ayyukan Zukata