إعدادات العرض
1- Manzon Allah SAW ya kasance yana anbaton Allah a kowane yanayi yake
2- Da wannan aka Umarce ku? cewa ku riqa jifan littafin Allah da Shashinsa? kuma Al-ummai sun vata kafinku a irin wannan, lallai ku ba komai bane a cikin irin wannan, ku dubi abunda aka Umarceku da shi, kuma ku yi aiki da shi, wanda kuma aka haneku to ku hanu
3- Kada kuyi jayayya a cikin Qur'ani saboda Jayayya a cikinsa Kafirci ne
4- sun kasance suna koyan ayoyi goma daga Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi -, ba sa koyan wasu goman daban har sai sun san abinda ke cikin wadannan na ilimi da aiki
5- Manzon Allah SAW ya ce mun: Ka karanta mun Al-qur'ani, sai na ce: ya manzon Allah yaya zan karanta maka bayan kai aka saukarwa? ya ce: Ni ina son inji Qur'ani daga wani na"
6- Lallai cewa a cikin littafin da Manzon Allah SAW ya rubuta zuwa Amr Bn Hazm lallai cewa kada wanda ya tava Qur'ani sai yana da tsarki
7- An tambayi Ibn Abbas da Muhammad Bn Al-hanafiyya: shin Annabi SAW ya bar wani abu? sai suka ce: babu abunda ya bari banda abunda yake tsakanin Bangwaye biyu
8- Ku karanta Al-qur'ani abunda zukatanku suka fahimta, to idan kuma kuka sava to ku tashi ku barshi
9- Abubuwa biyu nafi tsoro ga Al-umma ta Al-qur'ani da kuma Nono, Amma tsorona da nono saboda zasu riqa bin kauyuka kuma suna bin son ransu kuma suna barin Sallah, kuma Al-Qur'ani shi ne Munafukai su koyeshi sai su riqa jayayya da muminai da shi