إعدادات العرض
1- Ku rika Tilawar Alqurani Na Rantse da wanda raina yake a Hannunsa yafi saurin guduwa sama da Rakumi a cikin Dabaibayinsa.
2- Mafi Alkairinku wanda ya koyi Al'qu'ani kuma ya koyar da shi
3- Duk wanda ya karanta wani harafi daga littafin Allah, to, yana da lada, kuma kowane lada za a ninkashi goma
4- Kwatankwacin muminin da yake karanta AlKur'ani kamar gawasa ne, kanshinta mai dadi ne, kuma dandanonta mai dadi ne, kuma kwatankwacin muminin da ba ya karanta AlKur'ani kamar dabino ne ba shi da kanshi amma dandanonsa ma zaki ne
5- Gangaran wajen Karatun Quran yana tare da Manyan Mala'iku Masu biyayya ga Allah, kuma wanda yake karatu kuma yake guragura a cikinsa yana mai shan wuya to yana da lada biyu.
6- Za'a ce da ma'abocin Alkur’ani: Karanta ka daukaka, ka rera kamar yadda ka kasance kana rerawa a duniya, domin cewa matsayinka zai tasayane a karshen ayar da ka karantata
7- Babu hassada sai a cikin mutum biyu: mutumin da Allah ya bashi kudi, sai ya yi mulkin halakar sa da gaskiya, da kuma mutumin da Allah ya bashi hikima da shi, don haka ya yanke hukunci ya kuma koyar da shi
8- Ranar Al-kiyama za'a zo da Qur'ani da Ma'abotansa wadan da suke aiki da shi a cikin Duniya
9- Lallai cewa Allah yana daga Darajar wasu Mutane da wannan littafin kuma ya sauke Darajar wasu
10- Tir da xayansu da yake cewa Na manta Aya kaza da kaza, aa an mantar da shi ku riqa tuna Qur'ani, saboda shi ne mafi saurin mantawa daga zukatan Maza sama da Raquma
11- Ku karanta Alqurani domin zai zo Ranar Alkiyama mai ceton Ma'abotansa