إعدادات العرض
1- Ya Allah kada Ka maida kabarina gunki
2- Wanda ya rantse da wanin Allah to hakika ya kafirta ko ya yi shirka
3- Lallai cewa mafi tsoron abinda nake jiye muku tsoro karamar shirka" suka ce : Mece ce karamar shirka ya Manzon Allah? ya ce: "Riya
4- Shin ba haramta abin da Allah ya halatta suke ba sai kuma ku haramta shi? kuma su halarta abin da Allah ya haramta kuma ku halarta shi ba? sai na ce:e. sai ya ce wannan shi ne ibadarsu.
5- cewa an tambayi Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - game da ambulaf? Ya ce: Aikin Iblis ne.
6- Wanda camfi ya mayar da shi ga barin bukatarsa; to hakika ya yi shirka suka ce menene kaffarar hakan? ya ce: Ka ce ya Allah! babu wani alheri sai alhairinka, kuma babu camfi sai dai abin da ka nufa, kuma babu abin bauta da cancanta in ba kai ba
7- Wanda ya gamu da Allah ba ya tarayya da shi da wani to zai shiga Aljanna, wanda kuma ya gamu da shi yana shirka da shi to zai shiga wuta
8- Daga Dan Abbass cikin fadin Allah inda yake cewa: kuma suka ce kada ku kuskura ku bar Allolinku kuma kada ku bar Waddan da Suwa'an da kuma Yagusa da ya'uka da kuma Nasra, sai ya ce wadan nan sunayen na wasu Mutanen kikrki ne daga cikin Mutanen Annabi Nuh, yayai da suka Mutu sai shaidan yayi musu wahayi ga Mutanensu kan su kafa a wurarensu da suke zama gumaka, kuma su sa musu sunansu sai kuwa suka yi, kuma ba'a bauta musu ba sai bayan wadan nan sun Mutu kuma an manta da Ilimin sai aka rika bauta musu"
9- Allah madaukaki yana cewa: {Don haka kada ku sanya wa Allah kima, duk da cewa kun sani.} Ibn Abbas ya fada a cikin ayar cewa: "Aboki: shirka ne, wanda aka boye daga tururuwa da ke dauke da bakar leda a cikin duhun dare.
10- Canfi shirka ne, canfi shirka ne, canfi shirka ne, - sau uku -", babu wani a cikinmu saidai, saidai cewa Allah - Mai girma da daukaka - Yana tafiyar da shi da dogara (ga Allah)
11- Wanda ya rantse da amana to baya daga cikinmu