إعدادات العرض
FALALOLI DA LADUBBA
FALALOLI DA LADUBBA
1- Dukkan ayyuka basa yi yiwuwa sai da niyyoyi, kuma kowanne mutum yana da ladan abin da ya niyyata ne
2- Lallai halal a bayyane yake kuma haram ma a bayyane yake
4- Ɗayanku ba zai yi imani ba, har sai ya sowa ɗan uwansa abinda yake sowa kansa
5- Lallai Allah Ya wajabta kyautatawa akan kowanne abu
9- Imanin ɗayanku ba zai cika ba har sai son zuciyarsa ya kasance mai bi ga abin da na zo da shi
13- Kada harshenka ya gushe yana ɗanye daga ambatan Allah
14- Shin ba na ba ku labarin mafi girman zunubai ba?
15- Idan mutum ya so dan'uwansa to ya sanar da shi cewa shi yana sonsa
16- Manyan zanubai su ne: Yi wa Allah shirka, da saɓawa iyaye, da kashe rai, rantsuwa mai dulmiyarwa
18- ((Ku nisanci abubuwa bakwai masu halakarwa
21- Allah Zai shigar da shi Aljanna akan aikin da yake akansa
25- Aljanna ita ce mafi kusa daga dayanku daga igiyar takalminsa, wuta ma tamkar hakan
28- An kewaye wuta da sha'awowi, kuma an kewaye Aljanna da abubuwa ki
34- Idan musulmai biyu suka haɗu da takubbansu, to, wanda ya kashe da wanda aka kashe suna cikin wuta
35- Lallai halal a bayyane yake kuma haram ma a bayyane yake
36- Lallai Allah Ya wajabta kyautayi a kan kowane abu
37- Allah ba Ya duba zuwa surorinku da dukiyoyinku, sai dai Yana duba zuwa zukatanku da ayyukanku
39- Kada ka yi fushi
41- Wani bawa ya aikata wani zunubi, sai ya ce: Ya Allah Ka gafarta min zunubina
43- Wanda aka haramtawa sauƙi to an haramta masa alheri
46- Na haneku da zato; domin cewa zato shi ne mafi karyar zance
48- Kowa ne aikin alheri sadaka ne
49- Kada ka wulaƙanta komai daga wani aikin alheri, ko da ka gamu da ɗan uwanka ne da sakakkiyar fuska
50- Mai ƙarfi ba shi ne gwanin kaye ba, kadai mai ƙarfi shi ne wanda yake mallakar kansa a yayin fushi
51- Wanda ya shiryar a kan wani alheri, to, shi ma yana da kwatankwacin ladan wanda ya aikatashi
52- Kada ku zagi matattu; domin cewa sun iso zuwa abin da suka gabatar
54- Mai yanke zumunci ba zai shiga aljanna ba
55- Annamimi ba zai shiga aljanna ba
58- Wanda ya kasance ya yi imani da Allah da ranar lahira, to, ya faɗi alheri ko ya yi shiru
59- Wanda ba ya jin ƙan mutane Allah - Mai girma da ɗaukaka - ba zai ji ƙansa ba
60- Lallai mafi ƙiyayyar mutane a wurin Allah (shi ne) mai taurin kai mai tsananin husuma
66- Kalmomi guda biyu masu sauƙi a harshe, masu nauyi a ma'auni, masu soyuwa ga Ubangiji Al-Rahman
67- Babu wani abu mafi girma a wurin Allah - Maɗaukakin sarki- sama da addu'a
68- Wanda ya kare mutuncin ɗan uwansa Allah Zai kare fuskarsa daga wuta a ranar al-ƙiyama
71- Wanda Allah yake nufin shi da alheri sai ya fahimtar da shi addini
72- Lalle Allah Yana son bawa mai tsoronSa, wanda ya wadatu, mai ɓoye kansa
73- Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya kasance ba ya ƙin karɓar turare
77- Lalle mumini yana riska da kyawawan dabi’unsa matsayin mai azumi da mai tsayuwar dare
78- Lalle masu kyawawan dabi’unku suna cikin zaɓaɓɓunku
79- Lalle Allah Yana jinkirtawa azzalumi, har idan ya kama shi ba zai taɓa kufcewa ba
80- Ban bar wata fitina a baya na ba mafi cutar da Maza kamar mata ba
81- Ku sauƙaƙa kada ku tsananta, ku yi bushara kada ku yi kora
85- Wanda ya karanta ayoyi biyu na ƙarshen Suratul Bakara da daddare sun ishe shi
88- Masu jin ƙai (Ubangiji) Al-Rahman yana jin ƙansu, ku ji ƙan mutanen ƙasa wanda ke sama zai ji ƙanku
90- Mun kasance a wurin Umar, sai ya ce: An hana mu ƙaƙale
92- Ya kai yaro, ka ambaci Allah, ka ci da damanka, ka ci abin da ke gabanka
98- Lallai cewa Allah zai tseratar da wani mutum daga al'ummata agaban halittu a ranar Alkiyama
